in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Kenya za ta karbi bakun taron dandalin bitar nasarorin da aka samu a fannin yaki da shan-Inna
2018-11-11 16:03:48 cri
Hukumar kula da harkokin kiwon lafiya ta MDD ta bayyana cewa, a mako mai zuwa ne idan Allah ya kai mu kasar Kenya tare da hadin gwiwar hukumar lafiya ta duniya(WHO) za su shirya taron bita kan irin nasarroin da aka samu a yaki da cutar shan-Inna a nahiyar Afirka.

Taron hukumar yaki da cutar shan-Inna ta Afirka(ARCC) zai gudana ne a birnin Nairobin kasar Kenya daga ranar 12- 16 ga watan Nuwanban da muke ciki, inda za a yi bitar nasarorin da nahiyar ta samu game da kawar da kwayar cutar ta shan-Inna.

Yayin taron, ana saran kasashen nahiyar guda bakwai da suka hada da Kamaru da Najeriya da Guinea-Bissau da Jamhuriyar Afirka ta Tsakiya da Sudan ta kudu da Equatorial Guinea da Afirka ta kudu za su gabatar da rahoto game da irin matakan da suka dauka na ganin bayan cutar.

Najeriya ce kasa daya tilo a nahiyar da har yanzu ke fama da cutar, yayin da ake kokarin hana yaduwarta a kasashe masu hadari kamar Nijar, da Kenya da Somaliya da Jamhuriyar demokiradiyar Congo.

Wakilin hukumar lafiya ta MDD a Kenya Rudi Eggers, ya yaba da irin ci gaban da kasashen na Afirka suka samu game da kawar da cutar shan-Inna, amma kuma ya jaddada cewa, hanya mafi muhimmanci ta hana sake bullo cutar ita ce kara sanya ido. (Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China