in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Yawan mutanen da suka mutu sanadiyar wasu hare-haren ta'addanci da aka kai a Somaliya ya karu zuwa 50
2018-11-11 15:36:11 cri
Wasu kafofin 'yan sanda da na asibiti a kasar Somaliya na cewa, yawan mutanen da suka kwanta dama sanadiyar wasu hare-haren ta'addanci guda uku da aka kai birnin Mogadishu a ranar Jumma'a ya karu zuwa 50, yayin da wasu mutane 58 kuma ke samun kulawar raunukan da suka ji a asibitoci daban-daban dake birnin.

Wani jami'in 'yan sanda da ya bukaci a sakaye sunansa ya shaidawa kamfanin dillancin labarai na Xinhua cewa, an gano karin gawawwaki karkashin baraguje, lamarin da ya kai ga karuwar wadanda suka mutun zuwa 50. Yana mai fargabar cewa, watakila akwai karin mutane da kasa ta danne, amma dai suna iya bakin kokarinsu na ganin sun gano wadanda suka bace.

A ranar Jumma'a da rana ne dai wasu manyan bama-baman suka tashi a kusa da mahadar kilomita 4, inda ake zargin maharan Al-shabaab da auna otel din Sahafi da 'yan siyasa suka fi zama kana wani wuri mai tsaro da a baya 'yan jaridu ke yawan zuwa don dauko rahotanni game da yakin basasar kasar ta Somaliya.

Hotunan daga wurin da lamarin ya faru na nuna baragujen motoci warwatse a kan hanyar. Sai dai kuma MDD da wasu kasashen ketare sun yi Allah wadai da hare-haren, wadanda ke zuwa 'yan watanni bayan da kasar Somaliyar ke cika shekara guda da harin bam din da aka kai cikin wata babbar mota a ranar 14 ga watan Oktoban shekarar 2017, harin da ya yi sanadin mutuwar sama da mutane 500.

A halin da ake ciki, ita ma tawagar kungiyar tarayyar Afirka dake aikin tabbatar da zaman lafiya a Somaliya(AMISON) ta yi Allah-wadai da hare-haren da aka kai a kan otel din na Sahafi da ma hedkwatar leken asirin kasar dake birnin Mogadishu mai fama da tashin hankali.

A cikin wata sanarwa da ta fitar jiya Asabar a birnin Mogadishu, tawagar ta AMISON ta lashi takwabin karfafa sintiri tare da gwamnatin Somaliya da nufin murksuhe 'yan ta'adda da ma ragowar kungiyoyin 'yan tawaye.(Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China