in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An sace dalibai 79 da malamai 3 a yankin Kamaru mai amfani da Turancin Ingilishi
2018-11-06 11:03:04 cri
Ministan yada labarai na Kamaru, Issa Tchiroma, ya ce an sace yara 79 da malamai 3, da yammacin ranar Lahadi a yankin arewa maso yammaci, daya daga cikin yankunan kasar da masu amfani da Turancin Ingilishi suka fi rinjaye, wanda kuma ke fama da rikici.

Issa Tchiroma, wanda kuma shi ne kakakin gwamnatin kasar, ya ce an dauki dukkan matakai daga bangarorin farar hula da soji, domin tabbatar da an dawo da daliban da malamansu cikin koshin lafiya, ya na mai cewa ana binciken tungar wadanda suka sace su.

Wata majiya daga jami'an tsaro ta shaidawa Xinhua cewa, an sace daliban da malamansu ne daga wata makarantar sakandare mai zaman kanta mai suna Presbtyterian dake yankin Nkwen na Bamenda, babban birnin yankin arewa maso yammacin kasar.

Minsitan ya ce masu satar mutanen za su nemi kudin fansa, domin shi ne dalilin mummunan aikin na su.

Wani fitattacen shugaban 'yan aware Eric Tataw, ya fitar da wani bidiyo a baya-bayan nan, wanda ya nuna dalibai 11 a tsorace, inda 'yan aware dauke da makamai ke yi musu tambayoyi. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China