Issam Daalees, daya daga cikin shugabannin kungiyar Hamas dake tsakiyar zirin Gaza, shi ne ya tabbatar da hakan a wata sanarwar da aka rabawa manema labarai.
Da yake tsokaci game da yunkurin shiga tsakani wanda hukumar tattara bayanan sirri ta kasar Masar ke yunkurin shiryawa, Daalees ya ce za'a ci gaba da yin wancan yunkurin shi ma "har sai mun kai ga cimma matsaya wadda ta yi daidai da muradun al'ummarmu."
Tun da farko a wannan rana, wata tawagar wakilan Misrawa ta isa zirin Gaza ta hanyar Erez wadda ta ratsa kasar Isra'ila domin maido da tattaunawar sulhu da bangarorin Palastinawa dangane da batun yarjejeniyar zaman lafiya da Isra'ila.
Wata kafar yada labarai ta cikin gida ta ce, wakilan sun gudanar da tattaunawa tare da wasu manyan jami'an kungiyar Hamas da sauran shugabannin daya bangaren domin cimma matsaya na duba yiwuwar tsagaita bude wuta tsakanin Isra'ila da mayakan kungiyar Hamas a zirin Gaza. (Ahmad Fagam)