in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sudan ta kudu zata shiga tsakani don tattaunawa tsakanin gwamnatin Sudan da 'yan tawaye
2018-11-06 10:49:27 cri
Kasar Sudan ta kudu ta mika bukatar neman shiga tsakani domin tattaunawar sulhu tsakanin makwabciyarta gwamnatin kasar Sudan da kungiyoyin 'yan tawayen kasar ta Sudan, 'yan watanni kadan ke nan bayan da Khartoum ta shiga tsakani wajen cimma yarjejeniyar zaman lafiya.

Tut Gatluak, mashawarci na musamman ga shugaban kasa kan harkokin tsaro, ya fadawa 'yan jaridu a jiya Litinin cewa, gwamnatin Sudan da kungiyoyin 'yan tawayen kasar sun amince da tayin da Juba ta yi musu na shiga tsakani don tattaunawar sulhun, wanda ake sa ran gudanarwa a makon gobe.

Kasar ta Sudan ta jima tana fuskantar rikici da kungiyoyin 'yan tawaye masu fafutukar ceto al'ummar Sudan wato (SPLM-N) a kudancin Kordofan da jahar Blue Nile tun a shekarar 2011.

An sha yunkurin shirya tattaunawar sulhu a lokuta da dama da nufin kawo karshen tashin hankalin dake cigaba da ta'azzara a yankunan biyu na kan iyakokar Sudan da Sudan ta kudun amma al'amarin ya ci tura. (Ahmad)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China