in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
MDD ta bukaci hawa teburin sulhu don warware rikicin arewacin Somalia
2018-11-06 10:40:59 cri
Wakilin MDD a Somalia, Nicholas Haysom, wanda ya kammala ziyarar yini biyu a arewacin kasar da yammacin ranar Lahadi, ya bukaci a warware rikicin yankin cikin ruwan sanyi.

Nicholas Haysom, wanda shi ne manzon musamman na Sakatare Janar na MDD a Somalia, ya yi kira da a wareware rikicin da ake a garin Tukaraq na yankin Sool da ake takkadama a kai, cikin ruwan sanyi.

Cikin wata sanarwa da ya fitar jiya, jami'in ya ce ya gana da shugabannin yankunan biyu, inda suka tattauna kan batutuwa daban-daban, ciki har da yankin da ake rikici a kai.

An fara samun rikici a Tukaraq ne tun cikin watan Junairu, bayan dakarun Somaliland sun yi arangama da takwarorinsu na Puntland, dangane da neman iko da yankin na Sool.

Jihohin biyu na Somalia, sun sha karawa tun shekarar 2002 dangane da neman iko da yankunan arewacin kasar da suke takkadama a kai. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China