in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Mambobin kasashen BRICS zasu karfafa mu'amalar al'adu
2018-11-01 11:09:35 cri
Kasashen Brazil, Rasha, India, Sin da Afrika ta kudu, wato mambonin kasashen BRICS, a jiya Laraba sun sanya hannu kan yarjejeniyar zurfafa hadin gwiwa a fannin raya al'adu.

Ministocin raya al'adu na kasashen BRICS sun sanya hannu kan yarjejeniyar ne a Johannesburg, bayan shafe watanni suna tuntubar juna. Yarjejeniyar zata tabbatar da kasashen 5 sun karfafa hadin gwiwarsu a bangaren raya al'adu, da fannin ado da kwalliya. Ministan al'adu na kasar Afrika ta kudu Nathi Mthethwa ya bukaci a gaggauta aiwatar da yarjejeniyar.

Ministocin raya al'adun sun amince zasu shigar da sabon bankin raya cigaba domin samar da kudaden da za'a yi amfani dasu wajen ayyukan raya al'adu da ayyukan fasahar gargajiya. Sannan sun amince da kafa kwamitin aikin raya al'adu na BRICS wanda zai kunshi manyan jami'ai daga kasashen na BRICS, domin bunkasa mu'amala tsakanin mutum da mutum da karfafa hadin gwiwar kamfanoni fasahar kirkire kirkire.

Mataimakin ministan raya al'adu da yawon shakatawa na kasar Sin Xiang Zhaolun ya bayyana cewa, al'adu wani muhimmin bangare ne a hadin gwiwar BRICS. Zai kara samar da fahimtar juna a tsakanin mambobin kasashen BRICS, kuma zai inganta bangaren yawon bude ido da kawo babbar moriya ga tattalin arziki. Ministocin sun kuma amince da kafa wani tsari na hadin gwiwa tsakanin cibiyoyi. (Ahmad)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China