in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Merkel tana son bunkasa zuba jari a Afrika
2018-10-31 15:52:25 cri

Shugabar gwamnatin Jamus Angela Merkel ta sanar a jiya Talata cewa tana son bullo da sabbin hanyoyin karfafa zuba jarin kasar Jamus a nahiyar Afrika.

Da take jawabi a lokacin babban taron tattalin arziki a birnin Berlin, Merkel ta yi alkawarin cewa, gwamnatin Jamus za ta samar da karin kudade ga kamfanonin kasarta a matsayin inshora domin kaucewa barazanar siyasa da haddarorin dake cikin harkokin cinikayya a kokarin kyautata cinikin Jamus a kasashen waje.

A shekarar da ta gabata, Merkel ta kaddamar da wani gagarumin shiri da nufin fadada hanyoyin zuba jarin kasarta a Afrika a matsayin wani bangare na manufofin fadar shugaban kasar Jamus karkashin shiri cinikayya karkashin kungiyar G20. Domin kyautata dangantakar tattalin arziki a tsakaninta da kasashen Afrika a matakin farko, Jamus tana ci gaba da daukar matakai na sassauta kudaden inshora a kanana da matsakaitan masana'antun cikin gida (SMEs), a yayin da take yin mu'amalar ciniki da kasashe da shiyyoyin duniya da suka rattaba hannu kan sabuwar yarjejeniyar cinikayyar. (Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China