in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Rundunar sojin Aljeria ta gano makaman yaki a kusa da iyakar kasar da Mali
2018-10-30 10:09:28 cri
Dakarun Aljeria, sun lalata wasu makaman yaki, ciki har da na'urar kakkabo makami mai linzami, yayin wani aikin yaki da ta'addanci da suka gudanar a kusa da iyakar kasar da Mali.

Wata sanarwa da ma'aikatar tsaron kasar ta fitar, ta ce dakarun da aka tura yankin kudancin kasar na Bordj Badji Mokhtar, dake kusa da iyakar kasar da Mali ne suka gano dimbin makaman.

Makaman sun hada da tankokin kakkabo makami mai linzami 4 da babbar bindiga kirar Machine Gun da wasu bindigogi masu kwarya-kwaryar sarrafa kai da gurneti 2 da alburusai 2,984 nau'ika daban daban.

Sanarwar ta ce aikin ya nuna irin jajircewa da sa ido na dakarun da aka tura kan iyaka, domin tabbatar da tsaron yankunan kasar da kuma dakile duk wani yunkuri na fasakaurin makamai ko yi wa tsaro da zaman lafiyar kasar tarnaki. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China