in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An bude taron harkokin zuba jari a Geneva, inda aka jadadda hadin kai kan muradun ci gaba masu dorewa
2018-10-23 10:44:43 cri
An kaddamar da taron harkokin zuba jari na duniya na 2018 jiya Litinin a Geneva, inda masu jawabi yayin bude taron, suka yi kira da a mayar da hankali kan yanayin rashin tabbas da ake ciki yanzu, tare da hada kai tsakanin gwamnatoci da bangarori masu zaman kansu wajen cimma muradun ci gaba masu dorewa.

Dandalin inganta cinikayya da ci gaba na MDD UNCTAD ne ke shirya taron na manyan jami'ai da kan gudana bayan shekaru 2, domin magance batutuwan da suka shafi zuba jari.

Sakatare Janar na dandalin UNCTAD Mukhisa Kituyi, wanda ya ce tattalin arzikin duniya na cikin yanayi na rashin tabbas fiye da shekaru 10 da suka wuce, ya ce taron da zai gudana daga ranar 22 zuwa 26 ga wata, ya samu mahalarta 6,000, ciki har da shugabannin kasashen 12 da kuma shugabannin kamfanoni masu zaman kansu sama da 50.

Ya kara da cewa, suna neman yadda za a magance kalubalen da ake fuskanta da lalabu manufofi, ta yadda za a mayar da hankali da hadin kai tsakanin shugabanni, kan damamakin dake tattare da tattalin arzikin duniya maimakon matsalolin da yake da su.

Ya ce shawo kan wadancan kalubale na da muhimmanci ga ci gaban duniya a hanyoyin cimma muradun ci gaba masu dorewa na MDD ya zuwa shekarar 2030.

Mukhisa Kituyi ya ce taron zai taimaka wajen tsara manufoofin da za su taimaka wajen sauya manufofin zuba jari na duniya, ta yadda za su dore. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China