in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Erdogan da Trump sun amince a yi cikakken bayani kan mutuwar dan jaridar Saudi
2018-10-22 09:17:29 cri
Shugaban kasar Turkiyya Recep Tayyip Erdogan da takwaransa na kasar Amurka Donald Trump sun tattauna ta wayar tarho a daren ranar Lahadi game da mutuwar dan jaridar kasar Saudiyya Jamal Khashoggi.

A lokacin zantawar tasu ta wayar tarho, sun cimma matsaya cewa duk wanda aka samu da hannu a mutuwar dan jaridar wajibi ne a gurfanar da shi a gaban shara'a, kakakin shugaban kasar Turkiyya ne ya bayyana hakan cikin wata sanarwa.

Erdogan tun da farko ya fada a ranar Lahadi cewa, zai yi cikakken bayani game da batun mutuwar Khashoggi a ranar Talata a lokacin da zai gana da 'yan jam'iyyarsa a majalisar dokoki.

Marigayi Khashoggi, dan jaridar kasar Saudiyya ne, an dena jin duriyarsa tun bayan da ya shiga karamin ofishin jakadancin Saudiyya dake birnin Istanbul a ranar 2 ga watan Oktoba.

A ranar Asabar da ta gabata masarautar Saudiyya ta sanar da cewa Khashoggi ya mutu ne a sanadiyyar barkewar fada a karamin ofishin jakadancinta, amma ba ta yi cikakken bayani kan masabbabin mutuwar dan jaridar ba. (Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China