Kakakin rundunar 'yan sandan jihar, Yakubu Sabo Abubakar ne ya tabbatar da adadin ga kamfanin dillanci labarai na Xinhua, inda ya ce rikicin ya barke ne tsakanin matasan kabilar Hausa da ta Adara.
Rahotanni sun ce lamarin ya auku ne sanadiyyar sabanin da aka samu kan inda 'yan kasuwa za su rika sauke kayayyakinsu na sayarwa ranar Alhamis da ake cin kasuwa a kauyen Kasuwa Magani, wanda ke da nisan kilomita 31 daga birnin jihar.
Yakubu Abubakar ya kara da cewa 'yan sanda sun cafke mutane 22 dake da alaka da tashin rikicin. (Fa'iza Mustapha)