in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Saudiyya ta tsare mutane 18 dangane da mutuwar dan jaridar kasar da ya bata
2018-10-20 16:01:14 cri
Kamfanin dillancin labarai na Kasar Saudiyya (SPA), ya ruwaito cewa, gwamnatin kasar ta tsare mutane 18 dangane da mutuwar dan jaridar kasar da ya bace wato Jamal Khashoggi.

Binciken farko da ofishin mai shigar da kara na kasar ya gabatar, ya bayyana cewa, fada ta kaure tsakanin Jamal Khashoggi da wadanda ya hadu da su a ofishin jakadancin Saudiyya dake Instanbul, al'amarin da ya kai ga mutuwarsa.

Ofishin ya kuma tabbatar da cewa za a ci gaba da gudanar da bincike game da lamarin, yana mai cewa za a hukunta dukkan wadanda ke da hannu.

A baya dai, Saudiyya ta sha musanta zargin da ake wa masarautar kasar na kashewa ko tsare Khashoggi. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China