Netanyahu ya yi wannan gargadi ne a lokacin taron majalisar zartaswar Isra'ilan a Jerusalem.
Firaiministan ya yi wannan gargadi ne a sakamakon karuwar tashe tashen hankula wanda Palestinawa ke tada boren a kusa da wani shingen jami'an tsaro dake zirin Gaza.
A ranar Juma'ar da ta gabata, wasu mutane 15,000 suka yi zanga zanga a kusa da shingen jami'an sojojin, inda suka kona tayoyi da kuma girke duwatsu a kan titi, kana da yin amfani da abubuwan fashewa da gurneti da suka dinga jefan dakarun tsaron Isra'ilan.
A lokacin boren, kamar yadda wata majiya daga Palestinawa ta rawaito, an kashe mutane 7 daga cikin masu zanga zangar, da suka hada da mutane 3 wadanda suka tsallaka shingen da dakarun sojojin Isara'ilan suka kafa. (Ahmad)