Wata sanarwar da ofishin hukumar dake birnin Tripolin Libya ya fitar, ta ce, bisa alkaluman watannin Yuli da Agustan bana da aka bayar, akwai bakin haure sama da dubu dari shida daga kasashe da yankuna 41 wadanda ke makale a Libya, akasarinsu 'yan kasashen Nijar da Masar da Chadi da Sudan da kuma Najeriya.
Sanarwar ta kuma ce, hukumar kula da kaura ta duniya na hadin-gwiwa da gwamnatin kasar Libya, a wani kokari na mayar da bakin hauren kasashensu bisa radin kansu. (Murtala Zhang)