in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An mika ta'aziyya ga mutanen da suka mutu a sakamakon gobarar motar jigilar mai
2018-10-07 16:20:59 cri
Shugaban kasar Congo Kinshasa Josef Kabila ya sanar ta gidan telebijin din kasar a daren ranar 6 ga wata cewa, an ware kwanaki uku a kasar a matsayin makoki don nuna alhini ga mutanen da suka mutu a sakamakon gobarar da aka samu a kan motar jigilar mai a birnin Kisantu dake kudu maso yammacin kasar Congo Kinshasa.

Kabila ya bayyana cewa, za a gudanar da bincike kan wannan batu, tare da gudanar da ta'aziyya ga mutanen da suka mutu a sakamakon gobarar.

A ranar 6 ga wata da safe, wata motar jigilar mai ta yi karo da wata babbar mota dake tsaya a gefen titi, wanda ya haddasa samun gobara a motar jigilar mai, inda gobarar ta yi ta bazuwa cikin sauri. Ya zuwa yanzu, yawan mutanen da suka mutu a sakamakon hadarin ya karu zuwa 50 ko ma fiye.

An ce, bayan da hadarin ya faru, mai ya dinga malala, mutanen dake kewaye sun yi ta kwasar man. Daga baya, gobara ta kama motar jigilar mai bayan da ta fashe, gobarar ta bazu a motoci da gine-ginen dake kewayen ta.

Bayan faruwar hadarin, tawagar MDD mai aikin kiyaye zaman lafiya dake kasar Congo Kinshasa sun tura motocin likitanci domin kai dauki ga mutanen da suka ji rauni tare da kwashe su zuwa asibitin birnin Kinshasa. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China