in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An kaddamar da ginin titin da ya hada Mozambique da Tanzania
2018-10-03 15:55:54 cri
Shugaban Mozambique Filipe Nyusi, ya jagoranci aza harsashin ginin titin lardin Cabo Delgado dake arewacin kasar, wanda zai hada kasarsa da makwabciyarta Tanzania.

A jawabin da ya gabatar, shugaba Filipe Nyusi, ya bayyana ginin titin a matsayin cikar buri na bai daya na tsoffin shugabanni da jama'ar kasashen biyu.

Bankin raya nahiyar Afrika ne ya samar da kudin ginin titin da ya kunshi ginin gadoji uku, da za su saukaka zirga-zirgar mutane da hajoji, tare kuma da bada gudummawa ga harkar yawon bude ido, wanda ake sa ran zai bunkasa tattalin arzikin yankin.

Shugaban ya kara da cewa, titin zai bunkasa cinikayya a kasar, da ma wadda ake yi tsakaninta da makwabciyarta Tanzania, tare kuma da taimakawa wajen rage fatara.

Rukunin kamfanin gine-gine na Anhui Foreign Economic Construction na kasar Sin ne zai gudanar da aikin, inda kuma zai dauki yawancin ma'aikatansa a yankin. Shugaban ya bukaci wadanda za a dauka aikin su kasance masu kwazo. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China