in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Yawan wadanda suka mutu sakamakon girgizar kasa da tsunami a Indonesiya ya karu zuwa 832
2018-09-30 16:06:46 cri
Rahotanni daga kasar Indonesiya na cewa, yawan wadanda suka mutu sakamakon bala'in girgizar kasa mai karfi da kuma tsunami wadanda suka afkawa lardin Sulawesi dake tsakiyar kasar ranar Jumma'a, ya karu zuwa 832, ana kuma fargabar adadin zai iya karuwa.

Mai magana da yawun hukumar kula da bala'u ta kasar Sutopo Purwo Nugroho shi ne ya sanar da hakan, yana mai cewa, girgizar kasa ba kakkautawa masu karfin maki 6.0 da 7.4 gami da tsunami mai karfin maki 6.1 ne suka yi kaca-kaca da lardin. Sai dai bala'in ya fi shafar wani yanki a Palu, babban birnin lardin da kuma gundumar Donggala.

Kakakin ma'aikatar watsa labarai da sadarwa na kasar Ferdinandus Setu ya ce, a jiya Asabar babban filin jirgin saman lardin yana gudanar da ayyukan jin kai ne kawai. Haka kuma na'urorin sadarwa a sassan daban-daban na lardin suna aiki yadda ya kamata. (Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China