in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
AU ta karrama jami'an 'yan sanda bisa gudunmuwar da suka bayar ga wanzuwar zaman lafiya a Somalia
2018-09-29 16:51:15 cri
Shirin wanzar da zaman lafiya ta Tarayya Afrika dake aiki a Somalia wato AMISOM, ta karrama jami'an 'yan sanda 30 da aka tura kasar, domin bunkasa yunkurin wanzar da zaman lafiya, saboda irin rawar da suka taka.

A karshen makon nan ne 'yan sanda da suka fito daga kasashen Kenya da Zambia da Uganda da Saliyo, za su bar kasar dake kahon Afrika, bayan shafe shekara 1 suna aiki karkashin shirin na AMISOM.

Cikin wata sanarwa da ta fitar, mukaddashiyar Kwamishinan 'yan sandan AMISOM Chritine Alalo, ta jadadda muhimmiyar rawar da 'yan sandan suka taka, wajen karawa rundunar 'yan sandan Somalia karfi, dake iya aiwatar da ayyukan tsaron al'umma bisa kwarewa.

An ba jami'an wadanda suka gudanar da ayyuka na musammam, lambar yabo a Mogadishu, saboda namijin kokarin da suka yi da gudunmuwar da suka bayar ga wanzuwar zaman lafiya a Somalia. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China