in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kudurori 8 na taron FOCAC za su tallafawa Afirka, in ji shugaban jamhuriyar Afirka ta tsakiya
2018-09-27 10:24:07 cri

Shugaban Jamhuriyar Afirka ta tsakiya Faustin-Archange Touadera, ya ce an cimma gagarumar nasara a taron dandalin hadin gwiwa tsakanin Sin da kasashen nahiyar Afirka da ya gudana a birnin Beijing, kana kudurorin nan 8 da aka ayyana yayin taron, za su kara agazawa nahiyar wajen cimma manyan nasarori.

Shugaba Faustin-Archange Touadera ya bayyana hakan yayin da yake zantawa da kamfanin dillancin labarai na Xinhua, yana mai cewa kudurorin wadanda suka hada da bunkasa raya masana'antu, da samar da manyan ababen more rayuwa, da bunkasa cinikayya da zuba jari ba tare da gurbata muhalli ba, na da matukar muhimmanci. Shugaban ya ce yana matukar sha'awar yadda Sin ke ba da tallafin kwarewa ga kasashen Afirka.

Ya kara da cewa, idan ana son gina kasa, dole ne a fara da samar da horo na kwarewar aiki. A wannan fanni kasar Sin ta taimakawa Afirka da dabarun sanin makamar aiki. Hakan a cewar sa mataki ne da ya dace matasan nahiyar su yi na'am da shi.

Game da tasirin bashin Sin ga kasashen Afirka kuwa, Mr. Touadera ya ce nahiyar na bukatar kudaden gina ababen more rayuwa, duba da cewa idan ba bu kudade, zai yi wuya kasashe kamar jamhuriyar Afirka ta tsakiya su samu damar bunkasuwa. Don haka a cewar sa bashin da Sin ke samarwa muhimmin taimako ne ga kasashen nahiyar. (Saminu Hassan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China