in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Dakarun Kenya sun kashe mayakan al-Shabab 10 a gabar tekun kasar
2018-09-25 11:02:00 cri
A wani labarin kuma, a kalla mayakan al-Shabab 10 dakarun kasar Kenya (KDF) suka hallaka da yammacin ranar Litinin a lokacin wani samame da suka kaddamar a maboyar 'yan ta'addan dake gabatar tekun yankin Lamu.

Paul Njuguna, kakakin rundunar tsaro ta KDF, ya bayyana a cikin wata sanarwa cewa, an yi mummunan gumurzu tsakanin dakarun tsaron da mayakan al-Shabab inda dakarun na Kenya suka samu nasarar hallaka mayakan a arewacin Pandaguo dake shiyyar Lamu na kasar Kenya.

Bayan hallakan mayakan na Alshabaab 10, sojojin sun kuma gano bindigogi kirar AK47 guda 7, da alburusai. Sojojin suna ci gaba da farautar sauran mayakan da suka tsere da raunuka a jikinsu, in ji jami'in. (Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China