A ranar Alhamis ne ma'aikatar harkokin wajen kasar Amurka, ta bayyana shirin kasar na kakaba takunkumai ga sashen samarwa, da bunkasa kayan aiki na hukumar koli ta ayyukan sojin kasar Sin, da kuma daraktan sashen, tana mai zargin Sin da karya dokokin gwamnatin tarayyar kasar, dokokin da ke sanya Amurkan daukar matakai masu tsauri. (Saminu Alhassan)