in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Sin ta bayyana kudurin na hada kai da sauran kasashen duniya a fannin kare hakkin dan-Adam
2018-09-19 10:43:31 cri
Mamba a hukumar siyasa na kwamitin koli na JKS, kana shugaban sashen wayar da kan jama'a na kwamitin koli na JKS Huang Kunming ya bayyana kudurin kasarsa na hada kai da dukkan masu ruwa da tsaki a fannin kare hakkin dan-Adam duk da irin gagarumar nasarar da ta cimma a wannan fanni .

Huang Kunming ya bayyana hakan ne jiya Talata yayin da yake jawabi a taron dandalin kare hakkin dan-Adam na wannan shekara da aka bude a birnin Beijing na kasar Sin.

Ya ce, har kullum JKS da ma gwamnatin kasar na mutunta da kuma kare hakkin dan-Adam. Yana mai cewa a cikin sama da shekaru 40 da suka gabata, kasar Sin ta hade manufofi da suka shafi batun kare hakkin bil-Adam da yanayin da kasar ke ciki a zahiri

Dandalin da aka fara shiryawa a shekarar 2008, a bana ya samu halartar jami'ai da masana da muhimman mutane sama da 200 daga kimanin kasashe da yankuna 50 da ma kungiyoyin kasa da kasa.(Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China