Sin na fatan gudanar da hadin gwiwa da sassan duniya a fannin kare hakkokin bil Adama
Wani babban jami'in JKS mai mulkin kasar Sin, ya ce Sin ta cimma gagarumar nasara a tarihin ta, musamman a fannin kare hakkokin bil Adama, tana kuma shirye ta yi hadin gwiwa da sauran jam'iyyu dake sassan kasashen duniya a bangare kare hakkokin dan Adam.
Huang Kunming, wanda mamba ne a ofishin siyasa na kwamitin tsakiyar JKS, kana shugaban sashen yada bayanai na kwamitin tsakiyar jam'iyyar, shi ne ya yi wannan tsokaci, a taron dandalin tattaunawa game da hakkokin dan Adam na bana, wanda aka bude a nan birnin Beijing a Talatar nan. (Saminu Alhassan)