in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Adadin wadanda suka mutu sanadiyyar cutar kwalara a Zimbabwe ya karu zuwa 30
2018-09-18 10:44:04 cri
Ministan lafiya da kula da yara na Zimbabwe Obadiah Moyo, ya ce adadin mutanen da suka mutu sanadiyyar cutar kwalara ya karu zuwa 30, yayin aka samu rahoton mutane 5,463 da suka kamu da cutar.

Obadiah Moyo, ya ce gwamnati da majalisar gudanarwa ta birnin Harare da 'yan sanda, na iyakar kokarin takaita yaduwar cutar da ta barke makonni 2 da suka gabata a yankunan Glen View da Budiriro masu yawan jama'a.

Tun daga lokacin ne kuma, cutar da ake samu daga ruwa mara tsafata, wadda aka ayyanawa matakin ta-baci, ta yadu zuwa sauran sassan kasar.

An samu barkewar cutar ne sanadiyyar fashewar bututun kawar da najasa, wanda ya bata ruwan rijiyar burtsatsai da wasu daga cikin mazauna yankunan ke amfani da shi.

Ministan ya ce suna kara kai ruwa da magunguna yankunan da cutar ta barke, biyo bayan tallafin da suka samu daga abokan hulda daban-daban.

A cewar Ministan kananan hukumomi July Moyo, la'akari da yanayin bukatar gaggawa na lafiya, tuni ma'aikatarsa ta shawarci shugaban kasar Emmerson Mnangagwa ya ayyana matakin ta baci kan annobar. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China