in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Masani: Alakar Sin da Afirka zai taimakawa nahiyar da al'ummarta
2018-09-16 15:12:53 cri
Darektan makarantar Confusius na jami'ar Egerton dake kasar Kenya, Mohamed Hussein Abdille ya bayyana cewa, alakar dake tsakanin Sin da Afirka za ta amfanawa nahiyar da ma al'ummominta, sabanin yadda kasashen yammacin duniya ke sukar hadin gwiwar sassan biyu.

Mohamed Hussein Abdille wanda ya bayyana hakan yayin zantawa da kamfanin dillancin labarai na Xinhua a baya-bayan nan, ya ce, sakamakon goyon bayan da kasashen nahiyar suka samu daga kasar Sin, yanzu haka shugabanin kasashen nahiyar suna iya tafiyar da harkokin kasashensu ba tare da tuntubar tsoffin kasashen da suka yi musu mulkin mallaka ba.

Yayin da alakar sassan biyu ke ci gaba da bunkasa a 'yan shekarun nan, wasu kasashen yammacin duniya na cewa, kasar Sin na jibgawa kasashen Afirka bashi ne, domin ta samu tasiri na siyasa da ma kwashe albarkatun da Allah ya horewa nahiyar

Jamai'in ya ce gwamnatin kasar Sin ba ta taba tilastawa kowa ce kasa karba rance ba. Gwamnatocin kasashen Afirka ne suka sanya hannu kan yarjeniyoyin rance bisa radin kansu domin gudanar da ayyukan raya kasashen su.

Ya ce, kasashen nahiyar sun dade suna karbar tallafi da rance daga kasashen yamma, amma nahiyar ba ta samu ci gaba kamar yadda take a halin yanzu ba. Bugu da kari, kasashen yamma sun sha gallazawa kasashen na Afirka a lokacin da suke yi musu mulkin mallaka. (Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China