in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Wakilin Sin a MDD ya yi kira da a karfafa hadin-gwiwar kasa da kasa ta fannin yaki da cin hanci da rashawa
2018-09-12 11:12:17 cri
Zaunannen wakilin kasar Sin dake majalisar, Ma Zhaoxu ya yi kira da a inganta hadin-gwiwar kasashen duniya don yaki da cin hanci da rashawa. Ma Zhaoxu ya yi kiran ne a wajen wani taron da kwamitin sulhu na Majalisar Dinkin Duniya ya kira dangane da batun cin hanci da rashawa da rikici.

A jawabin da ya gabatar, jakada Ma ya ce, cin hanci da rashawa tamkar makiyi ne ga jama'ar fadin duniya. Haka kuma rage duk wani yunkuri na bayar da cin hanci da karbar toshiya gami da kara karfin maido da dukiyoyin da aka sata, na daga cikin muradun neman ci gaba da MDD ke son cimmawa nan da shekara ta 2030. Ma ya ce, ya zama dole kasashen duniya su rubanya kokarin karfafa hadin-gwiwa don yaki da cin hanci da rashawa, ta yadda ba za'a iya baiwa mutane damar bayar da cin hanci da karbar toshiya ba.(Murtala Zhang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China