Kafofin jami'an tsaro da na kiwon lafiya a kasar Somaliya na cewa, a kalla mutane shida ne suka game da ajalinsu, kana wasu 16 kuma suka jikkata, sakamakon wani harin kunar bakin wake da aka kai hedkwatar gundumar Hodan a Mogadishu.
Jami'in 'yan sandan Abukar Mohamed ya shaidawa kamfanin dillancin labarai na Xinhua cewa, dan kunar bakin waken ya kutsa da motar cikin hedkwatar gundumar Hodan, inda ya kashe mutane a kalla shida.
Darektan ayyukan ba da agajin gaggawa Abdikadir Abdirrahman ya shaidawa Xinhua cewa, a kalla mutane 16 ne aka garzaya da su asibiti. Yayin da shaidun gani da ido suka bayyana cewa fashewar ta yi barna.
Tuni dai kungiyar 'yan ta'adda ta al-Shabab ta dauki nauyin kai harin na baya-bayan nan.(Ibrahim)