in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Firaiministan Sin ya gana da shugaban Najeriya
2018-09-06 09:57:52 cri
Firaiministan kasar Sin Li Keqiang a jiya Laraba ya gana da shugaban Najeriya Muhammadu Buhari bayan kammala taron kolin FOCAC na Beijing 2018.

Da yake tsokaci dangane da batun kyautata alakar tattalin arziki da karfafa mu'amala tsakanin kasashen biyu, Li ya ce kasar Sin a shirye take ta bayar da duk wani taimako don bunkasa ci gaban Najeriya, ya ce kyakkyawar hadin gwiwar dake tsakanin kasashen biyu wajen raya cigaban bangarorin biyu tare, ya kara karfafawa kamfanonin kasar Sin gwiwa wajen shiga takarar neman ayyuka a Najeriya musamman a fannonin zuba jari da cinikayya, da samar da kayayyaki da kuma aikin gina kayayyakin more rayuwa ta hanyar bin ka'idojin ciniki domin bangarorin biyu su samu kyakkyawan sakamako na cin moriyar juna.

Shugaba Buhari ya taya wa kasar Sin murnar samun nasarar karbar bakuncin taron kolin FOCAC na Beijing kana ya yabawa kasar Sin saboda taimakon da take bayarwa wajen kyautata rayuwar bil adama, da horas da matasa, da taimakon da take baiwa Najeriya wajen zamanantar da aikin gona, da aikin gina kayayyakin more rayuwa. Ya ce Najeriya a shirye take ta kara zurfafa mu'amalar hadin gwiwar tsakaninta da kasar Sin. (Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China