in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Dunkulewar Sin da Afirka za ta inganta bunkasuwar Sin da Afirka cikin hadin gwiwa, in ji ministan wajen Nijar
2018-09-05 09:57:00 cri


A ranar 3 da 4 ga watan nan da muke ciki ne, aka kira taron kolin FOCAC a birnin Beijing, fadar mulkin kasar Sin. Babban taken taron shi ne "Yin hadin gwiwa domin cimma moriyar juna, hada kanmu domin karfafa dunkulewar kasashen Sin da Afirka". Cikin zantawarsa da wakilin sashen Hausa na CRI, ministan harkokin wajen kasar Nijar Kalla Hankourao wanda ya zo birnin Beijing domin halartar taron ya bayyana cewa, batun karfafa dunkulewar kasashen Sin da Afirka cikin hadin gwiwa da shugaban kasar Sin Xi Jinping ya ambata a yayin bikin bude taron, yana da muhimmiyar ma'ana, kuma tabbas zai ciyar da bunkasuwar kasashen Sin da Afirka gaba. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China