in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Babu "matsalar bashi" a Afirka, in ji shugaban bankin raya kasashen Afirka
2018-09-04 20:40:01 cri
Yau Talata, shugaban bankin raya kasashen Afirka Akinwumi Adesina, ya bayyana a yayin taron ganawar shugabannin kasashen Sin da Afirka, da wakilan harkokin masana'antu da cinikayya karo na 6 cewa, babu "matsalar bashi" a nahiyar Afirka.

Akinwumi Adesina ya ce, cikin shekarun baya bayan nan, yawan bashin dake cikin ma'aunin tattalin arziki na GDP na kasashen Afirka ya dan karu kadan, kuma adadin ya kai kashi 22 bisa dari a shekarar 2010, wanda ya karu zuwa kashi 37 bisa dari a shekarar 2017. Amma adadin bai kai kashi 100 bisa dari, ko kashi 150 bisa dari, kamar yadda kasashe masu ci gaba suke ba. Kana bai kai kashi 50 bisa dari na wasu kasashe masu samun saurin bunkasuwar tattalin arziki ba.

A yayin da yake tsokaci kan batun cewa wai "kasar Sin tana kara matsa wa kasashen Afirka lamba ta hanyar ba su bashi", Akinwumi Adesina ya jaddada cewa, bisa halin da kasashen Afirka suke ciki a yanzu, wato ana samun karuwar tattalin arziki cikin yanayin zaman karko, da kuma karuwar yawan al'umma, kasashen Afirka suna bukatar taimako na kyautata ababen more rayuwarsu, don haka suke samun bashi bisa bukatunsu na neman jari, a maimakon sayen kayayyaki. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China