in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Masani: Taron kolin FOCAC na Beijing ya bude sabon babi a alakar Sin da Afirka
2018-09-04 13:35:59 cri
Darektan cibiyar nazarin harkokin kasar Sin dake Abuja, babban birnin Najeriya Charles Onunaiju ya bayyana cewa, taron kolin hadin gwiwar Sin da kasashen Afirka dake gudana yanzu haka a birnin Beijing na kasar Sin ya bude wani sabon babi a dangantakar Sin da Afirka ta hanyar ingantawa da zamanintar da ababen more rayuwa a nahiyar.

Jami'in wanda ya bayyana hakan cikin wata zantawar da kamfanin dillancin labarai na Xinhua, ya ce alakar sassan biyu, dangantaka ce ta moriyar juna ba wai ga kasar Sin kadai ba har ma ga duniya baki daya.

Onunaiju ya ce, shawarar ziri daya da hanya daya ta sanya kyakkyawar makoma ga taron na FOCAC, kuma hakan abu ne mai muhimmanci ga nahiyar Afirka. Yanzu haka kasar Sin ta sake sanar da aiwatar da wasu sabbin matakan raya alaka da kasashen Afirka guda 8 wadanda suka hada da fannonin raya masana'antu, da ababan more rayuwa da saukaka harkokin cinikayya da kare muhalli, dukkansu ana fatan aiwatar da su nan da shekaru uku masu zuwa da ma nan gaba.

Ya ce, wadannan sabbin matakai za su taimaka matuka wajen raya nahiyar. Don haka ya shawarci shugabannin kasashen na Afirka da su inganta manufofinsu ta yadda za su ci gajiyar sabbin matakai da shirye-shiryen. (Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China