Shugaban kasar Najeriya ya yabawa hadin gwiwar dake tsakanin Sin da Afirka
A jiya ne aka gudanar da taron shugabanni da wakilan 'yan kasuwan Sin da Afirka a nan birnin Beijing. A jawabin da ya gabatar a madadin kasashen yammacin Afirka, shugaban kasar Najeriya Muhammad Buhari ya bayyana cewa, wannan ne karo na farko da dukkan kasashe membobin kungiyar ECOWAS suka halarci taron koli na FOCAC, yana fatan za a kara daukar matakan saukaka samun takardar visa da sauransu, da kuma zurfafa hadin gwiwa da yin mu'amala a tsakaninsu da kasar Sin a fannin al'adu da sauransu bisa shawarar "ziri daya da hanya daya" a wannan yanki. (Zainab)
Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku