in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ana yin shawarwari tsakanin shugabannin kasashe masu halartar taron kolin Beijing na FOCAC
2018-09-04 11:02:38 cri
A yau Talata 4 ga wata ne, ake yin shawarwari tsakanin shugabannin kasashe dake halartar taron kolin Beijing na dandalin tattaunawa kan hadin gwiwar Sin da Afirka wato FOCAC na shekarar 2018 a babban dakin taron jama'ar kasar Sin.

Shugaban kasar Sin Xi Jinping da shugaban kasar Afirka ta Kudu Matamela Cyril Ramaphosa za su shugabanci shawarwari da safe da kuma yamma daya bayan daya, inda shugabannin kasashen Sin da Afirka za su yi musayar ra'ayoyi kan bunkasuwar dangantakar dake tsakanin bangarorin biyu da batutuwan kasa da kasa da na yankuna da suke sa lura. Bugu da kari ana sa ran zartas da Sanarwar Beijing kan neman raya makoma ta bai daya tsakanin Sin da Afirka da kuma Shirye-shiryen Beijing na FOCAC daga shekarar 2019 zuwa 2021 a yayin taron. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China