Kamfanin dillancin labarai na KUNA na kasar, ya ruwaito Sarkin na jajantawa Shugaban Nijeriya Muhammadu Buhari, ya na mai kuma bayyana yadda Kuwait ke adawa da duk wani nau'in ta'addanci.
Da yake yi wa wadanda suka jikkata fatan samun lafiya cikin gaggawa, Sarki Sabah Al-Ahmad ya ce harin ya sabawa dukkan dokokin jin kai.
Akalla sojojin Nijeriya 30 mayakan Boko Haram suka kashe a wani hari da suka kai wa sansanin sojin dake kusa da iyakar kasar da Niger. (Fa'iza Mustapha)