Shugaban kasar Sin Xi Jinping ya bayyana cewa, nan da shekaru uku masu zuwa, kasar Sin za ta taimakawa Afirka wajen raya ayyuka 50 na samun ci gaba ba tare da gurbata muhalli ba da masu kiyaye muhalli. Kuma za ta mai da hankali kan yin hadin gwiwa da cudanya tare da Afirka a fannonin sauyawar yanayi da teku da shawo kan kwararowar hamada da kiyaye dabbobi da tsirrai. Sa'an nan za ta sa kaimi ga gina cibiyar hadin kan Sin da Afirka ta fuskar muhalli, da ma raya cibiyar gora ta bangarorin biyu, a kokarin taimakawa Afirka wajen raya sana'ar gora. (Kande Gao)