in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
#FOCAC#Xi Jinping: Sin na fatan karfafa al'umma mai kyakkyawar makoma ga dukkan al'umomin Sin da Afirka
2018-09-03 17:34:10 cri
A yayin taron kolin Beijing na FOCAC, shugaban kasar Sin Xi Jinping ya bayyana cewa, kasarsa na fatan kafa al'umma mai kyakkyawar makoma ga dukkan al'umomin Sin da Afirka bisa daukar nauyi tare, da samun nasara tare, da samar da alheri tare, da raya al'adu tare, da kuma tabbatar da tsaro da zaman lafiya tare.

Kamata ya yi, Sin da kasashen Afirka su karfafa tattaunawar siyasa da cudanyar manufofi a matsayi daban daban, da kara hada kai a sabbin fannoni, da raya sabbin fannoni na tattalin arziki, kana da samar da hakikanin nasarori ga jama'ar bangarorin biyu, da kuma kara yin mu'amala a fannonin al'adu, fasaha, ba da ilmi, da wasannin motsa jiki da dai sauransu. Baya ga haka, ya kamata a tsaya tsayin daka kan goyon bayan kasashen Afirka da wasu kungiyoyin shiyyar, ciki har da AU, don su warware matsalolinsu bisa hanyar da ta dace da su, haka akwai bukatar bangarorin biyu su karfafa hadin kai a fannin sauyin yanayi da sauran fannoni da suka shafi kiyaye muhalli. (Bilkisu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China