#FOCAC# Xi Jinping:An cimma gaggaruman nasarori a shirye-shirye goma na hadin gwiwar Sin da Afirka
Shugaban kasar Sin Xi Jinping a yau Litinin ya bayyana a nan birnin Beijing cewa, tun bayan taron kolin dandalin hadin kan Sin da Afirka FOCAC da aka gudanar a shekarar 2015 a birnin Johannesburg na kasar Afirka ta kudu, kasar Sin ta aiwatar da manyan shirye-shirye goma na hadin gwiwar Sin da Afirka kamar yadda ta alkawarta, ta kuma cika alkawarinta na samar da kudin tallafi na dala biliyan 60, a yayin da aka gama gina hanyoyin dogo da na mota da dama, baya ga wasu da har yanzu ake kan ginawa. Baya ga haka, sassan biyu na aiwatar da hadin gwiwa a fannonin kimiyya da ilmi da kiwon lafiya da saukaka fatara da sauransu. (Lubabatu)
Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku