in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
#FOCAC#Xi Jinping ya ce sam kasar Sin ba za ta yi abun da bai dace ba yayin hadin-gwiwarta da kasashen Afirka
2018-09-03 17:16:03 cri
Shugaban kasar Sin Xi Jinping a yau Litinin ya bayyana cewa, hadin-gwiwar dake tsakanin kasar Sin da kasashen Afirka, hadin-gwiwa ce mai salon musamman kana ta samun moriyar juna. Ya ce yayin da kasar Sin ke kokarin karfafa hadin-gwiwa da kasashen Afirka, sam ba za ta yi abubuwan da ba su dace ba, yana mai cewa ba za ta tsoma baki kan yadda kasashen Afirka ke kokarin neman samun bunkasuwa ba, kuma, ba za ta yi shiga sharo ba shanu cikin harkokin cikin gidan kasashen Afirka ba, kana, ba za ta tilastawa kasashen Afirka amincewa da dukkanin ra'ayoyinta ba, kana kuma, ba za ta gindaya wani sharadin siyasa kan kasashen ba a yayin da take samar masu da tallafi, haka zalika, kasar Sin ba za ta nemi samun moriya ita kadai ba, yayin da take kokarin zuba jari a kasashen Afirka.(Murtala Zhang)
Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China