A gobe Litinin 3 ga wata ne, za a bude taron kolin dandalin tattaunawar hadin gwiwa a tsakanin Sin da kasashen Afirka, wato FOCAC a nan birnin Beijing. A yayin bikin bude taron, shugaban kasar Sin Xi Jinping zai gabatar da muhimmin jawabi, inda zai bayyana matakan da za a dauka domin tabbatar da kyakkyawar makomar al'ummar kasashen Sin da Afirka ta bai daya, tare kuma da sanar da matakan da za a dauka a gaba domin kara inganta hadin gwiwa a tsakanin sassan biyu.
A Gobe da safe, da misalin karfe 10 saura kwata, agogon Najeriya da Nijer, sashen Hausa na gidan rediyon kasar Sin zai watsa labarai game da bikin kai tsaye ta shafinta na yanar gizo da kuma Facebook. kada a manta, adireshinmu na kafofin su ne hausa.cri.cn/ da www.facebook.com/crihausaradio.