in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaban Zimbabwe ya ce zai ci gaba da kokarin karfafa hadin-gwiwa tsakanin kasarsa da kasar Sin
2018-09-02 17:10:12 cri

Kafin ya taso daga Harare zuwa nan birnin Beijing, don halartar taron koli na dandalin tattaunawa kan hadin-gwiwar Sin da Afirka wato FOCAC, shugaban kasar Zimbabwe Emmerson Mnangagwa ya zanta da 'yan jaridun kasar Sin, inda ya bayyana ra'ayinsa dangane da batutunwa da suka shafi tsarin dandalin FOCAC da dangantakar dake tsakanin kasashen Zimbabwe da Sin.

Mnangagwa ya ce, tsarin dandalin FOCAC ya samar da wani kyakkyawan zarafi ga kasashen Afirka wajen samun ci gaba, kana, a karkashin wannan tsari, gwamnatin kasar Sin ta samar da dimbin taimako da goyon-baya ga kasashen Afirka. Ya ce sabuwar gwamnatin Zimbabwe za ta yi amfani da damammakin da kasar Sin ta ba ta don neman samun ci gaba.

Wannan shi ne karon farko da Mnangagwa ya kawo ziyara kasar Sin tun bayan da ya lashe babban zaben kasar ta Zimbabwe, kana, karo na biyu da ya kawo ziyara kasar Sin a bana.(Murtala Zhang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China