Sanarwar da kakakin rundunar Col Onyeama Nwachukwu ya fitar, ta ce mayakan bataliya ta 2 ne suka yi bata kashi da 'yan tada kayar bayan.
Nwachukwu ya ce 'yan tada kayar bayan na tada fitina da karban kudi daga hannun mutane, sai dai sun fuskanci tirjiya daga dakarun Operation lafiya dole wadanda suka samu taimako daga takwarorinsu na sama.
Rahotanni sun ce akalla sojoji 30 ne mayakan Boko Haram suka kashe a ranar yayin bata kashin, sai dai kakakin rundunar sojin bai yi bayani dangane da rahoton ba. (Fa'iza Mustapha)