Shugabannin Ghana da Masar da Jamhuriyar Congo da Afrika ta Kudu za su kawo ziyara kasar Sin
Kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin Lu Kang, ya sanar a yau Juma'a cewa, Shugaban Ghana Nana Akufo-Addo da na Masar Abdel-Fattah al-Sisi da na Afrika ta kudu, Cyril Ramaphosa da na Jamhuriyar Congo, Denis Sassou Nguesso, za su ziyarci kasar Sin don halartar taron koli na dandalin tattaunawar Sin da Afrika.
Shugabannin za su zo ne bisa gayyatar da Shugaban Kasar Sin Xi Jinping ya yi musu, inda ziyarar tasu za ta fara daga yau 31 ga wata zuwa 9 ga watan Satumba. (Fa'iza Mustapha)