Sin: Za a kara yin hadin gwiwa tsakanin Sin da Afirka a fannin aikin soja
A yayin da ake shirin kaddamar da taron koli na dandalin hadin gwiwar Sin da Afirka FOCAC a mako mai zuwa a birnin Beijing na kasar Sin, Wu Qian, kakakin ma'aikatar tsaron kasar Sin, ya furta a yau Alhamis cewa, sojojin kasar Sin da na kasashen dake nahiyar Afirka suna da hulda mai kyau tamkar 'yan uwa. Haka kuma a nan gaba kasar Sin za ta ci gaba da taimakawa kasashen Afirka wajen tabbatar da tsaro bisa karfin kansu, da kara yin hadin gwiwa a fannin aikin soja a tsakanin bangarorin 2. (Bello Wang)
Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku