in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Hadin-gwiwar Sin da Afirka na samar da damammaki samun ci gaba ga Afirka
2018-08-30 11:04:15 cri
Mataimakiyar shugaban hukumar raya kasashe ta Majalisar Dinkin Duniya wato UNDP, wadda kuma ita ce shugabar ofishin hukumar dake kula da harkokin Afirka, madam Ahunna Eziakonwa, ta bayyana cewa, hadin-gwiwar da ake yi tsakanin kasashen Afirka da kasar Sin hadin-gwiwa ce ta samun moriyar juna, wadda za ta taimakawa kasashen Afirka wajen kara samun bunkasuwar tattalin arziki da zamantakewar al'umma.

Madam Ahunna na daya daga cikin jami'an tawagar MDD da za su zo birnin Beijing don halartar taron kolin dandalin FOCAC a farkon watan Satumba, karkashin jagorancin babban sakataren MDD Antonio Guterres.

Yayin da take zantawa da kamfanin dillancin labarai na Xinhua a kwanakin baya, Madam Ahunna ta ce, kasashen Afirka da kasar Sin na da kamanceceniya da yawa, abun da ya sa hadin-gwiwarsu ke tafiya yadda ya kamata. Ta ce jarin da kasar Sin ke zubawa a Afirka, musamman a fannin inganta muhimman ababen more rayuwar jama'a, na karfafawa kasashen Afirka gwiwar samun sabon ci gaba.

Yayin da take tsokaci kan batutuwan da ya kamata a maida hankali kai yayin da ake hadin-gwiwa tsakanin Sin da Afirka, Ahunna ta yi kira da a kara hada shawarar "ziri daya da hanya daya" da bukatun kasashe da yankunan Afirka daban-daban, ta yadda za'a kara samun sakamako mai kyau bisa hadin-gwiwar moriyar juna.(Murtala Zhang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China