in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaban Botswana ya baro kasarsa don halartar taron FOCAC
2018-08-30 09:23:21 cri

Shugaban Botswana, Mokgweetsi Masisi, ya baro kasarsa a jiya Laraba, domin ziyarar aiki da halartar taron koli na dandalin tattaunawar hadin gwiwar Sin da Afrika da za a yi a nan birnin Beijing na kasar Sin.

Da yake ganawa da manema labarai jiya a birnin Gaborone, mukadashin ministan harkokin wajen kasar Nonofo Molefhi, ya ce a matsayin Sin na kasa mai tasowa da ta samu ci gaba, ta kuduri niyyar karfafa dangantaka da kasashen Afrika domin kara taimaka musu, ta fuskar raya tattalin arziki da kyautata zamantakewa.

Ya ce, Botswana da kasar Sin na da hadin gwiwa a fannonin da suka shafi kiwon lafiya da gine-gine da saura abubuwan ci gaba, don haka, halartar taron FOCAC zai taimakawa kasashen biyu kara karfafa alakarsu.

Ya kara da cewa, taron zai ba kasashen Afrika dake da muradin bunkasa kansu, kyakkyawar dama ta morar kasar Sin ta hanyar koyon dabaru mabanbanta da ta yi amfani da su wajen samun ci gaba da inganta rayuwar al'ummarta. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China