in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ambaliyar ruwa ta haddasa mutuwar mutane 36 a jamhuriyar Nijar
2018-08-29 19:58:52 cri
Ofishin hukumar kula da aikin jin kai ta MDD dake Jamhuriyar Nijar ya sanar a jiya Talata cewa, ya zuwa ranar Litinin 27 ga wata, ambaliyar ruwa da ta abka wa Jamhuriyar Nijar ta haddasa mutuwar mutane 36 kana wasu fiye da dubu 130 na fama da radadin bala'in.

Sanarwar ta kara da cewa, tun a watan Yunin bana, sassa kasar ke fama da ambaliyar ruwa sakamakon ruwa kamar da bakin kwarya da ake ta shekawa. Yankunan da suka fi fama da bala'in sun hada da jihohin Agadez, Maradi, Zinder, da kuma Diffa. Alkaluman kididdiga na nuna cewa, ban da hallaka mutane, matsalar ta kuma haddasa lalacewar wasu gidaje fiye da 7200, da gonakin da fadinsu ya kai kadada 8162 da ruwa ya malale. (Bello Wang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China