Xi ya bukaci matasa da su shiga a dama da su wajen gina makomar bai daya ga daukacin bil-Adama
Shugaba Xi Jinping na kasar Sin ta yi kira ga matasa da su shiga a dama da su cikin aikin gina shawarar ziri daya da hanya daya, tare da goyon bayan hadin gwiwar Sin da kasashen Afirka, kana su ba da gudummawarsu wajen gina al'umma mai kyakkyawar makoma ga daukacin bil-Adama.
Xi ya bayyana hakan ne jiya Talata, lokacin da yake ba da amsa ga wasikar da mahalarta dandalin matasa na kasa da kasa game da kirkire-kirkire da al'adu wadanda hanyar siliki ta tsara, taron da ya gudana a biranen Changsha da Nanjing a watan Mayu. (Ibrahim Yaya)