in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Taron koli na Beijing na FOCAC na shekarar 2018 zai kara inganta hadin gwiwar dake tsakanin Sin da Afirka
2018-08-29 16:24:15 cri
Mataimakin shugaban kungiyar nazarin batutuwan Afirka ta kasar Sin Liu Hongwu ya bayyana a yau 29 ga wata cewa, taron koli na Beijing na FOCAC na shekarar 2018 da za a gudanar a watan Satumba zai kara inganta hadin gwiwar dake tsakanin Sin da Afirka.

Liu Hongwu ya bayyanawa 'yan jarida a wannan rana cewa, taron koli na Beijing na bana zai waiwayi ayyukan da aka gudanar bayan da aka kafa dandalin tattaunawar na FOCAC a cikin shekaru 18 da suka gabata, kana za a gabatar da shiri na raya Sin da Afirka na shekaru 3 masu zuwa har ma na tsawon lokaci, ta haka za a inganta dangantakar dake tsakanin Sin da Afirka zuwa wani sabon matsayi.

Liu Hongwu ya yi nuni da cewa, hadin gwiwar dake tsakanin Sin da Afirka da tsarin hadin gwiwa na kasa da kasa kamar shawarar "ziri daya da hanya daya", hadin gwiwar dake tsakanin kasashe masu tasowa, hadin gwiwar dake tsakanin kasashe membobin kungiyar BRICS zasu taimaka wajen cimma samun moriyar juna ta hadin gwiwar dake tsakanin Sin da Afirka tare da inganta hadin gwiwarsu zuwa wani sabon matsayi. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China