in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Wakilin MDD ya gayyaci kasashen duniya don tattauna batun rikicin Syria a wata mai zuwa
2018-08-29 11:05:55 cri

Kakakin MDD ya sanar cewa, wakilin musamman na MDD kan rikicin Syria ya gayyaci kasashen duniya masu yawa domin sun halarci taron tuntubar juna a ofishin MDDr dake Geneva a ranar 14 ga watan Satumba.

Wakilin musamman na MDD a Syria, Staffan de Mistura, ya gayyaci kasashen Masar, Faransa, Jamus, Jordan, Saudi Arabia, Birtaniya da kuma Amurka domin tattaunawar dake tafe, Stephane Dujarric, kakakin babban sakataren MDD Antonio Guterres ya bayyana hakan a taron manema labarai.

Wakilin musamman na MDD yana son yin amfani da wannan damar ce don tattaunawa tare da manyan wakilan wadannan kasashen game da matakai na gaba da za'a dauka domin warware rikicin kasar wanda kwamitin sulhun MDD mai lamba 2254 ya cimma matsaya kansa a shekarar 2015, wanda ya kunshi yunkurin MDDr wajen kafa kwamitin tsara kundin tsarin mulkin kasar Syria, da kuma daukar manyan hanyoyin tabbatar da shirin, in ji Dujarric.(Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China